Alhaji Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto shi ne Firimiyan jihar Arewa na farko kuma na ƙarshe.
Shi ne ya jagoranci gwamnatin jihar Arewa tun daga 1952 har zuwa 1966.
A wannan shekaru 14 ya aza harsashin duk wani ci gaban da ake tinƙaho da shi a yankin.
Amma fa ya gwada ƙarfin ikonsa akan abokan adawar siyasa na Arewacin Najeriya.
Sannan akuyarsa ta yi kuka wurin fafatawa da ƴan siyasar Kudancin Najeriya.
A ƙarshen rayuwarsa ya mayar da hankali kan haɓaka addinin Islama da musuluntar da Maguzawa.
Kuma Sojoji ƴan tawaye sun kashe shi ranar 15 ga Janairun 1966 a juyin mulkin da bai yi nasara ba.
Sai dai, har yanzu ba a samu wani mutum da ya maye gurbinsa a Arewacin Najeriya ba.
Негізгі бет Ойын-сауық Tarihin Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto
Пікірлер: 130