Matashiya Khadija Ɗantama ta bayyana yadda wata ƙawarta ta yi kutun-kutun ta rabata da saurayinta, lamarin da ya jefa rayuwarta cikin halin damuwa tsawon lokaci.
Ɗantama ta ce, ta yi nadamar yin rayuwa da ƙawar, kuma ta kan shiga cikin bacin rai duk lokacin da ta tuno lamarin.
A kashi na biyu na shirin "Yankan Ƙauna" na tashar Dala FM Kano, ta ce ba ta yi tsammanin hakan zata iya faruwa ba saboda yadda ta amince da ƙawartata.
Shin an taba cin amanarku a soyayya? kuma zaku iya shigowa cikin wannan shiri ta hanyar tuntuɓarmu ta wannan shafi.
Негізгі бет Yankan Kauna Ep 1: Na shiga tashin hankali lokacin da Ƙawata ta ƙwacemin saurayina - Khadija Ɗantama
Пікірлер: 20