A ranar 4 ga Fabrairun 2013 kotu ta tasa keyar Aminu Sule Lamido zuwa kurkuku.
Aminu Sule Lamido da ne ga tsohon gwamnan jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido, wanda ya mulki jihar daga 2007 zuwa 2015.
Hukumar EFCC ce ta gurfanar dashi a gaban babbar kotun tarayya dake Kano, karkashin mai shari'a Justice Fatu Riman.
EFCC dai ta zargi Aminu Sule Lamido da cuwa cuwa na rashin bayyana hakikanin kudin da ya dauka na dala dubu 50.
Tuhumar da aka karanta masa a kotu itace, a ranar 11 ga Disamban 2012 ya debi kudi dala dubu 50 daga Najeriya zuwa Cairo, wanda hakan ya saba da adadin da aka amince a hukumance na dala dubu 10 ga kowane dan Najeriya da zai fita kasar waje da tsabar kudi.
Hukumar EFCC dai ta ce wannan laifi ya saba da dokokin Najeriya musamman sashi na 2 uku cikin baka na dokar data haramta cuwa cuwar kudi ta 2011 da kuma sashi na biyu biyar cikin baka na ita wannan doka.
Sai dai a lokacin Aminu Sule Lamido ya musanta wannan zargi inda nan take lauyan sa ya nemi da a bashi beli.
Sai dai lauyan EFCC ya soki bukatar hakan, tare da neman kotu ta sanya wata ranar domin cigaba da sauraron karar.
Bayan da mai shari'a Justice Fatu Riman ta saurari kowane bangare ne kuma sai ta aike da Aminu Sule Lamido gidan yari.
A ranar 12 ga Yulin 2015 ne kotu ta same shi da laifi inda ta umarci a karbe kaso 25 na kudin da yaki bayyanawa.
A 2015 dinne kuma wata kotun tarayya da ke jihar Kano ta tura Aminu da dan uwansa Mustapha da mahaifin su Alhaji Sule Lamido, kurkuku bayan hukumar EFCC ta gabatar da su gaban ta.
EFCC ta ce ta gurfanar da Sule Lamido a gaban kuliya ne bisa zargin sama-da-faɗi da makuden kudade a lokacin mulkinsa.
EFCC ta zargi tsohon gwamnan da 'ya'yansa da yin cuwa-cuwar sama da N1.3 bn.
Негізгі бет A rana irin ta yau: Fabrairu 4, 2013 Aminu Sule Lamiɗo ya tafi kurkuku
Пікірлер